Miliyoyin Mutane Sun Halarci Jana’izar Imam Khaminaei A Qom Bayan Tehran

Miliyoyin mutanen Iran da kuma wasu daga kasashen waje ne suka halarci sallar Jana’izar Imam Sayyid Aliyul Khaminaei a masallacin Jamkaran dake wajen birnin Qom na ilmi a yau Talata. Tashar talabijan ta Presstv a nan Tehran ta bayyana cewa, Ayatullahi Abdullahi Jawadi Amuli ne ya jagoranci sallar jana’izar Imam Khaminaei da iyalansa inda miliyoyin […]
Mai Wakiltan Aya. Sistani Ne Zai Jagoranci Sallar Jana’iza Kan Imam Khaminaei A Birnin Karbala

Shugaban haramin Imam Hussain (a) a birnin Karbala na kasar Iraki ya bada sanarwan cewa, Al-Kabalaei ne zai jagoranci sallar Jana’izar Imam Khaminaei a birnin Karbala, a gobe Laraba da yamma, . Kamfanin dillancin labaran Tasnim news na kasar Iran ya nakalto majiyar ofishin Ayatullahi Sistani na cewa Babban malami kuma marja’I ba zai iya […]
Minsitan Harkokin Wajen Rasha Sergei Lavrov Zai Ziyarci Nijar A Gobe Laraba

Minsitan Harkokin Wajen Rasha SergeiLavrov zai ziyarci Jamhuriyar Nijar a gobe Laraba. Lavrov zai je Nijar ne don halartar taron ministocin harkokin waje karo na biyu tsakanin Rasha da Kawancen Kasashen Sahel wato (Mali, Nijar da Burkina Faso). A cewarsa, tawagar Rasha za ta yi la’akari da sakamakon tattaunawar da ta yi da Shugaban Hukumar […]
Iran Ta Yi Watsi Da Rahoton Da UAE Ta Mikawa Hukumar Zirga Zirgan Jiragen Ruwa Ta Duniya (IMO)

Gwamnatin kasar iran ta yi watsi da rahoton da UAE ta mikawa hukumar zirga zirgan jiragen ruwa ta duniya wato (Council of the International Maritime Organization (IMO) dangane da mashigar ruwa ta Hurmuz ta kuma kara da cewa UAE ta yi haka ne don siyasa da kuma matsin lamba daga wasu kasashe. Banda haka rahoton […]
Shugaban Kasar Amurka Ya Isa Turkiyya Don Halattan Taron Kungiyar Tsaro Ta NATO

Shugaban kasar Amurka Donal trump ya isa kasar turkiyya don halattan taron kungiyar tsaro ta NATO ta, inda bayan isarsa ya fadawa shugaban kasar turkiyya Rajab Tayyib Urdogan kan cewa, mai yuwa ya sayar masa jiragen yaki samfurin F-35 wadanda suka dade suna cece kuce a kan hakan, bayan da kasar Turkiyya ta saye garkuwan […]
Arakci: Matukar Ana Ci Gaba Da Yi Wa Iran Barazana To Babu Maganar Zama Akan Teburin Tattaunawa

Ministan harkokin wajen Jamhuriyar musulunci Dr. Abbas Arakci ya bayyana cewa; A karkashin nagare na 13 na takardar fahimtar juna a tsakanin Iran da Amurka, an bayyana cewa;matukar ana yi wa Iran barazana, to kuwa ba za a hau teburin tattaunawar karashe ba. Sayyid Abbas Arakci wanda ya halarci jana’izar jagora shahidi ya kuma ce; […]
Miliyoyin Mutane A Birnin Qum Suna Yin Bankwana Da Jagora Shahidi

A yau Talata miliyoyin mutanen birnin Qum su ka fito kwansu da kwarkwatarsu na layi mai tsawon kilo mita 7 daga masallacin Jamkaran zuwa haramin Fatima Ma’asumah ( a.s). Tashar talabijin din al’alam ta ambaci cewa; Ayatullah Jawad Amuli ne ya yi wa jagoran sallar jana’aza a masallacin Jamkaran tun da jijjifin safiyar yau Talata. […]
Syria: Bama-bamai Sun Fashe A Birnin Damascuss A Kusa Da Masaukin Shugaban Kasar Faransa

Rahotanni da suke fitowa daga birnin Damascuss na kasar Syria sun ambaci cewa; Wasu bama-bamai guda biyu sun tashi a kusa da ginin ma’aikatar yawon bude ido kuma kusa da masaukin shugaban kasar Faransa Emmanuel Macron da yake ziyarar aiki a Syria. Jim kadan bayan fashewar bama-bamai jami’an tsaro sun killace yankin da abin ya […]
Shugaban kasar Senegal Yana Shirin Kafa Sabuwar Jam’iyyar Siyasa

Shugaban kasar Senegal Bassirou Diomaye Faye yana Shirin kaddamar da sabuwar jam’iyyar siyasa bayan da sabani a tsakaninsa da Fira Minista Ousmane Sonko ya kara fadada. Wannan matakin na shugaban kasar yana zuwa ne gabanin kaddamar da zabukan kananan hukumomi da za ayi ba da jimawa ba da kuma kwaskwarimar da aka yi wa tsarin […]
Politico: Kungiyar Nato Tana Kara Jan Damarar Yiyuwar Fada Da Kasar Rasha

Jaridar Politico ta dauki labarin da yake cewa; kungiyar “Nato” tana karfafa bangarenta dake daura da Rasha domin yiyuwar barkewar fada a tsakaninsu. Jaridar ta ce hakan tana faruwa ne a daidai lokacin da mambobin kungiyar suke son rage dogaro da Amurka. Haka nan kuma jaridar ta ambaci cewa; Abinda yake faruwa shi ne kokarin […]
Wani Babban Jami’I A Kasar Iran Yace Jinin Jagora Ya Farkar da alumma Iran

Wakilin jagora a majalisar koli ta tsaron kasa, Ali Akbar Ahamadiyan ya bayyana cewa jini mai tsarki na jagoran juyin musulunci ya kara farkar da alummar iran kuma ya tunatar da su nauyin dake wuyansu na tunkarar wulakancin kasashe ma’abota girman kai na duniya A cikin wani jawabi da ya fitar a jiya litinin ya […]
MDD Ta Kafa Kwamitin Bincike Kan Cin Zarafin Fararen Hula A Kasar Sudan

Hukumar kare hakkin dan adam ta Majalisar DD , ta amince da kudirin dokar da ta yi Allah wadai da yadda dakarun RSF ke kara kai hare-hare a al-Obeid da ke Sudan, inda ta kafa kwamitin binciken gaggawa kan zargin cin zarafin da ake aikatawa a yankin. Birtaniya tare da wasu ƙasashe 14 ne dai […]
Yan Majalisar Dokokin Birtaniya Sun Bukaci Gwamnatin Ta Sanya Wa Natanyaho Takunkumi

Gwamman yan majalisar dokokin birtaniya sun yi kira ga gwamnati da ta kakabawa Binjemin Natanyaho fira ministan isra’ila takunkumi da sauran ministocinsa game da azabatar da falasdinawa fararen hula da gwamnatin isra’ila ke yi A cikin wata wasika da aka aike wa sakataren harkokin wajen birtaniya Yvette Cooper wanda akalla yan majalisar 71 suka sanyawa […]
Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran: Mutunci, Kishin kasa Su Ne Manyan Abin Gado Da Jagora Ya Bari

Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar iran Esma’ila Baqa’I ya fadi cewa manyan ababen gado da jagoran juyin musulunci na iran shahid Ayatullah Khamina’I ya bar wa Alummar iran shi ne mutunci, kishin kasam tsayin daka da kuma nuna juriya da jajircewa. A cikin wani sako da ya aike da shi ta shafinsa na X da […]
Falasdinawa 6 Ne Suka yi Shahada A Ci Gaba Da Keta Yarjejeniyar Dakatar Da Bude Wuta Da Isra’ila Ke Yi

Rahotanni da suka fito daga yankin falasdinu sun bayyana cewa akalla falasdinawa 6 sun yi shahada yayin da wasu guda 20 kuma suka jikkata a wani hari da sojojin HKI suka kai a yankin Gaza, a ci gaba da keta yarjejeniyar dakatar da bude wuta da suke yi da aka cimma tsakani A harin farko […]
Miliyoyin jama’a sun fita a titunan Tehran domin ban kwana da Ayatollah Seyyed Ali Khamenei

A Tehran Miliyoyin jama’a ne suka fito akan titunan Tehran a safiyar yau domin ban kwana da Jagoran juyin juya halin Musulunci na kasar, Ayatollah Seyyed Ali Khamenei, a ci gaba da tarurukan jana’iza da ake wa mirigayin. Titunan babban birnin Tehran, sun kasance cike makil da jama’a sanye da bakaken kaya dauke da jajayen […]
Iran : Pezeshkian zai halarci jana’izar Ayatollah Seyyed Ali Khamenei A Iraki

Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian zai yi tafiya zuwa Iraki a ranar Talata don halartar jana’izar Jagoran juyin juya halin Musulunci, Ayatollah Seyyed Ali Khamenei, wanda aka shirya gudanarwa a biranen Najaf da Karbala na Iraki a ranar Laraba. Ziyarar ta zo ne yayin da ake ci gaba da gudanar da jana’izar Jagoran da iyalansa […]
Tawagar Burkina Faso ta halarci taron Jana’izar Ayatollah Seyyed Ali Khamenei

Burkina Faso ta halarci tarurukan jana’izar Jagoran juyin juya halin Musulunci na Iran, Ayatollah Seyyed Ali Khamenei. Ministan Harkokin Wajen kasar ne ya jagoranci tawagar Burkinabe, wanda ya wakilci shugaban kasar, Kyaftin Ibrahim Traoré. Ministan Harkokin Wajen kasar Karamoko Jean Marie Traoré ya yi wa jama’a da gwamnatin Jamhuriyar Musulunci ta Iran ta’aziyyar Burkina Faso. […]
Gaza: Mutane 3 Sun Yi Shahada A Arewa Da Kudancin Gaza

A wani sabon harin da ‘yan sahayoniya su ka kai a cikin birnin Gaza, mutane 2 sun yi shahada, yayin da wani mutum daya ya yi shahada a Khan-Yunus. Bugu da kari harin na ‘yan sahayoniya ya yi sanadiyyar jikkatar wasu mutane 20 a birnin na Gaza da kuma Yanin Muwasi dake Khan-Yunus. Majiyar Asibiti […]
Sojojin Iran Sun Bayyana Cewa; Taron Jana’izar Jagora Shahidi Ya Farkar Da Duniya Akan Fada Da Masu Girman Kai

Mai Magana da yawun sojan Iran Amir Akrami Niya ya bayyana cewa; Al’ummar Iran ta kafa tarihi saboda yadda su ka fito a cikin miliyoyi domin yin bankwana da jagoran juyi shahidi Ayatullah Sayyid Ali Khamenei. Haka nan kuma ya ce abinda yake faruwa ya sauya zuwa wani yunkuri na farkar da al’ummar duniya akan […]