Yan Majalisar Dokokin Birtaniya Sun Bukaci Gwamnatin Ta Sanya Wa Natanyaho Takunkumi

Gwamman yan majalisar dokokin birtaniya sun yi kira ga gwamnati da ta kakabawa Binjemin Natanyaho fira ministan isra’ila takunkumi da sauran ministocinsa game da azabatar

Gwamman yan majalisar dokokin birtaniya sun yi kira ga gwamnati da ta kakabawa Binjemin Natanyaho fira ministan isra’ila takunkumi da sauran ministocinsa game da azabatar da falasdinawa fararen hula da gwamnatin isra’ila ke yi

A cikin wata wasika da aka aike wa sakataren harkokin wajen birtaniya Yvette Cooper  wanda akalla yan majalisar 71 suka sanyawa hannu  da suka fito daga jam’iyu daban daban ya nuna cewa cikakkun bayanai da aka gudanar game da Azabtar da falasdinawa da gwamnatin isra’ila ke yi  ya hada har da hannun fira ministan Banjemen natanyaho a ciki

Haka zalika yan majalisar sun bayyana cewa takunkumin da aka sanyawa wani minister a haramtacciyar kasar isra’ila Itamar ben Gvir a shekarar da ta gabata  da kuma Bazalel Smotrich  ya samu karbuwa sosai  kuma ya kawo canji kadan game da yadda gwamnatin isra’ila ke muamala da falasdinawa da take tsare da su

Mai bincike ta musamman ta majalisar dinkin duniya Francesca Albanese game da yanyin hakkin dan adam a yankin falasdinu ta fadi a cikin rahotonta ga hukumar kare hakkin bil adama ta majalisar dinkin duniya cewa yanayin  tsarin gidan yari Isra’ila ya koma tamkar wajen gwaje-gwaje na zalunci da aka kirkiro da suka kunshi ayyukan yi wa falasdinawa fyade da kwalabe, sandunan karfe, da kuma wukake.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted