Jagoran Juyin Juya Halin Musulunci Ya Jaddada Matsayin Iran Na Goyon Bayan Gwagwarmaya

Jagoran juyin juya halin Musulunci ya tabbatar da matsayin Jamhuriyar Musulunci mai cike da goyon bayan ‘yan gwagwarmaya Dangane da ƙa’idar hana kai hari da kuma ƙarfafa ƙa’idar ɗaukar fansa, Iran ta kai hare-haren makamai masu linzami kan wuraren soji a arewacin Falasɗinu da Isra’ila ta mamaye, don mayar da martani ga keta yarjejeniyar tsagaita […]
Shugaban Iran Ya Jaddada Cewa; Tsaron Al’ummar Iran Jan Layi ne

Shugaban kasar Iran ya jaddada cewa: Tsaron ‘yan ƙasa jan layi ne, kuma ba za su janye daga taruwa a sha tale-tale ko tattaunawa ba Shugaban kasar Iran Masoud Pezeshkian ya tabbatar da cewa: Gwamnatinsa ba za ta yi watsi da taruwan jama’a kan sha tale-talen kan hanyoyi ko kuma kauracewa teburin tattaunawa ba, yana […]
Kwamandan Rundunar Sojin Iran Ya Sanar Da Dakatar Da Yakin Da Ya Sake Kunno Kai Tsakanin Iran Da Isra’ila

Hedikwatar Rundunar Soji ta Tsakiya ta Khatam al-Anbiya ta sanar da dakatar da ayyukan soji kan sharudan doka Hedikwatar Rundunar Soji ta Tsakiya ta Khatam al-Anbiya ta Kasar Iran ta sanar da dakatar da ayyukan soji a kan abokan gaba ‘yan Sahayoniyya, tana mai jaddada cewa: Idan hare-haren suka ci gaba, musamman a kudancin Lebanon, […]
Rundunar Tsaron Juyin Juya Halin Musulunci Ta Sanar Da Martanin Da Ta Kai Kan Isra’ila

Rundunar tsaron juyin juya halin Musulunci ta kai hari da makami mai linzami a matsayin ramuwar gayya kan harin da aka kai wa daya daga cikin wuraren hakar mai na Iran Rundunar Tsaron Juyin Juya Halin Musulunci ta (IRGC) ta sanar a wata sanarwa a hukumance cewa: Dakarunta masu kula da makamai masu linzami sun […]
Kungiyoyin Gwagwarmayar Falasdinawa Sun Nuna Jin Dadinsu Da Harin Da Iran Ta Kai Kan Isra’ila

Kungiyoyin gwagwarmayar Falasdinawa Hamas da Jihadul-Islami sun yaba da martanin da Iran ta mayar kan laifuka da keta dokokin ‘yan mamaya Kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hamas, ta yaba da martanin da Iran da Yemen suka mayar kan Haramtacciyar kasar Isra’ila kan laifukan da take yi wa Lebanon da mutanenta, tana mai jaddada cewa: Mayar da […]
Gwamnatin Kasar Afrika Ta Kudu Ta Fara Shirin Hukunta Masu Nuna Kin Jinin Baki A kasar

Gwamnatin Afrika ta Kudu ta sha alashin daukar mataki mai tsauri kan masu nuna wariya da kuma kin jinin baki a fadin kasar, wanda ya zuwa yanzu an kwashe tsawon makonni ana rigimar korar baki a Afrika ta Kudu matakin da ya kai ga hallaka wasu bakin. Da yake jawabi a kafar Talabijin din kasar […]
Shugaban kasar Chin Ya kai Ziyara Koriya Ta Arewa A Daidai Lokacin Da Rikici Ke Kara Ruruwa A Fadin Yankin

Rahotanni sun bayyana cewa shugaban kasar china Xi Jinping ya ziyarci kasar koriya ta kudu a daidai lokacin da rikici yake kara Kamari a yankin domin kara karfafa dangantaka dake tsakanin kasashen biyu masu makwabtaka da juna, shugaban kasar China ya isa birnin Pyonyang babban birnin koriya ta Arewa ne a yau litinin inda ya […]
Dakarun Sojin Kasar Yamen Sun Sanar Da Haramtawa Jiragen Ruwan HKI Zirga-Zirga A Tekun Maliya

Rahotanni sun bayyana cewa dakarun sojin kasar yamen sun sanar cewa za su dauki mataken soji kan muradun HKI a yankin baki daya, kuma zai hada kai hare-hare da makamai masu linzami, kuma sun haramatawa jiragen ruwan Isra’ila motsi a fadin tekun bahar maliya, haka zalika rundunar sojin ta ce ayyukan soji za su ci […]
Ministan Wajen Kasar Iran Abbas Araqchi Ya Tattauna Da Takwarorinsa Na Yankin Kan Ci Gaban Da Aka Samu

Rahotani sun bayyana cewa ministan harkokin wajen kasar iran Abbas Araqchi ya tattaunawa ta wayar tarho da ministocin harkokin wajen kasashen yakin bayan martanin da kasar iran ta mayar kan HKI sakamakon hare-haren da ta kaddamar a yankin Dahiya na kasar Labanon. Ministan na iran yace ya tattauna ta wayar tarho da takwaransa na kasar […]
Ibrahim Riza’i: Wajibi Ne A Ladabtar Da Wannan Mahaukacin karen Mai Haushi ” Isra’il”

Tun a daren jiya ne dai Kakakin Kwamitin Tsaro a majalisar Shawarar Musulunci ta Iran Dr. Ibrahim Riza’i, ya bayyana cewa; Iran za ta mayar da martani akan harin da Haramtacciyar Kasar Isra’ila ta kai wa unguwar Dhahiya a cikin birnin Beirut, wanda kuma zai kasance mai tsanani. Ibrahim Riza’i ya kuma kara da cewa; […]
Lebanon: Mutane Biyu Sun Yi Shahada A Wani Harin Wuce Gona Da Iri Na “Isra’ila”A Birnin Beirut

Tashar talabijin din “Almayadin” mai watsa shirinta daga Lebanon ta watsa labarin dake cewa; Harin da ‘yan sahayoniya su ka kai wa unguwar Dhahiya a yau Lahadi da marece ya yi sanadiyyar shahadar mutane biyu da kuma jikkata wasu da dama. Wannan harin dai yana zuwa ne a matsayin ci gaba da keta hurumin kasar […]
Iran Ta Kai Wa Haramtacciyar Kasar Isra’ila Hari

A daren jiya ne dai dakarun kare juyin musulunci na Iran su ka fara kai wa arewacin Falasdinu dake karkashin mamaya hare-haren daukar fansa saboda kai wa birnin Beirut hari. A wata sanarwar da dakarun kare juyin musulunci su ka fitar, sun bayyana cewa; Sun kai harin ne akan sansanin sojan saman a Haramtacciyar Kasar […]
IRGC: Haramtacciyar Kasar Isra’ila Ta Kawo Wa Iran Hari Da Makamai Masu Linzami Samfurin “Ballistic”

Sanarwar da dakarun kare juyin musuluncin su ka fitar, ta kunshi cewa; Makiya sun kawo hari a kasarmu da safiyar yau Litinin ta hanyar amfani da makamai masu linzami samfurin “Ballastic”. A gefe daya wani kwararre akan harkokin tsaro dan kasar Iran Mukhtar Haddad ya ce; Da sani da kuma hadin bakin Amurka Haramtacciyyar kasar […]
Da Safiyar Yau Litinin Iran Ta Ci Gaba Da Kai Wa Haramtacciyar Kasar Isra’ila Hare-hare A Yankuna Mabanbanta

Rahotanni da suke fitowa daga Haramtacciyar Kasar Isra’ila sun ce, makamai masu linzamin da Iran ta harba sun sauka a yankunan Tel Aviv, Beit Shemish, da kuma Usdud. Bugu da kari, Iran din ta kai wa matsugunin ‘yan share wuri zauna na “Itmar” da aka gina a yammacin kogin Jordan hari, da ya haddasa tashin […]