Tashar talabijin din “Almayadin” mai watsa shirinta daga Lebanon ta watsa labarin dake cewa; Harin da ‘yan sahayoniya su ka kai wa unguwar Dhahiya a yau Lahadi da marece ya yi sanadiyyar shahadar mutane biyu da kuma jikkata wasu da dama.
Wannan harin dai yana zuwa ne a matsayin ci gaba da keta hurumin kasar Lebanon da Haramtacciyar Kasar Isra’ila take yi, wanda ya zuwa yanzu ya ci dubban rayukan mutanen kasa,musamman a kudancin kasar.
A gefe daya, kungiyar gwagwarmayar musulunci ta Hizbullah tana ci gaba da mayar da martani akan sojojin Haramtacciyar Kasar Isra’ila da suke mamaye da kudancin kasar.