Da Safiyar Yau Litinin Iran Ta Ci Gaba Da Kai Wa Haramtacciyar Kasar Isra’ila Hare-hare A Yankuna Mabanbanta

Rahotanni da suke fitowa daga Haramtacciyar Kasar Isra’ila sun ce, makamai masu linzamin da Iran ta harba sun sauka a yankunan Tel Aviv, Beit Shemish,

Iran ta yi gargadin kai hari kan duk jirgin sojin da ya yi yunkurin shiga Hormuz

Rahotanni da suke fitowa daga Haramtacciyar Kasar Isra’ila sun ce, makamai masu linzamin da Iran ta harba sun sauka a yankunan Tel Aviv, Beit Shemish, da kuma Usdud.

Bugu da kari, Iran din ta kai wa matsugunin ‘yan share wuri zauna na “Itmar” da aka gina a yammacin kogin Jordan hari, da ya haddasa tashin gobara. Haka nan kuma hare-haren na Iran sun isa zuwa Demona dake Naqab, sai kuma Bi’iru Sabaa.

Tashar talabijin din Aljazira ta ce, wasu gine-gine uku a matsugunin ‘yangsare wuri zauna na “Itamar” sun illata saboda faduwar makamai masu linzamin a kansu.

Miliyoyin ‘yan sahayoniya ne su ka gudu domin buya a karkashin kasa saboda hare-haren daga Iran.

A wani labarin na daban, kafafen watsa labarun Haramtacciyar Kasar Isra’ila sun ce, an kai wani harin da makami  mai linzami daga kasar Yemen.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted