Tsagerun Yahudawan Sahayoniyya ‘yan kaka gida sun kona wasu masallatai biyu
Tsagerun Yahudawan Sahayoniyya ‘yan kaka gida a yau Lahadi, sun kona wasu masallatan Falasdinawa guda biyu a biranen Nablus da Tulkarm da ke arewacin gabar tekun Yammacin Kogin Jordan.
A gefe guda kuma, sojojin mamayar Isra’ila sun fara wani kamfe na kama Falasdinawa da dama – ciki har da mata – tare da tsaurara matakan soji a yankuna daban-daban na Falasdinawa.
Shaidu ganin ido sun bayyana cewa: Tsagerun Yahudawan Sahayoniyyan ‘yan kaka gida sun kona Masallacin Al-Rahma – wanda a halin yanzu ake ginawa – a garin Qusra, kudu da Nablus, wanda ya haifar da hayaki daga ƙofofinsa, tagogi, da wasu abubuwan da ke cikinsa.
Wuta ta lalata wasu sassan masallacin da ke ƙauyen Kur kafin mazauna yankin su yi gaggawar zuwa don kashe ta tare da hana ta yaɗuwarta; a yayin harin kuma, wasu tsagerun yahudawan sahayoniyyan sun rubuta kalamai na nuna wariyar al’umma a jikin bangon masallacin.
Mahukuntan Falasdinawa sun yi Allah-wadai da wannan “mummunan hari na laifi,” inda suka bayyana cewa: An samu hare-hare guda 12 da sojojin mamaya da tsagerun Yahudawa suka kai kan masallatai a yankin Yammacin Kogin Jordan tun farkon shekara ta 2026.