rahotanni sun bayyana cewa sojojin Isra’ila sun kama falsdinawa guda 100 a fadin yankin gabar yammacin kogin jodan daga lokacin da aka fara Azumin watan Ramadan zuwa yanzu kamar yadda kungiyar kare hakkokin falasdinawa fursunoni ta bayyana.
A cikin wani rahoto da suka wallafa ya nuna cewa kungiyar ta pps ta ce binciken ya fara ne tun a ranar laraba da ta gabata lokacin da aka fara Azumin watan Ramadan, inda sojojin Isra’ila suka fara shiga cikin garuruwa da sansanin yan gudun hijira a cikin dare suna kama falasdinawa.
mata da dama da yara kanana suna daga cikin wadanda aka kama , a jiya lahadi ma sojojin Isra’ila sun kama falasdinawa guda 8 da suka hada da yara guda 3 a lokacin da suka kai samame a garin qalqiliya dake kusa da garin Azzun.
haka zalika sojojin Isra’ila sun tsaurara tsaro a shingayen sojoji tun daga farkon Ramadan . sama da shingayen soji na din din din dana wucin gadi guda 1000 ne suke takaita zirga zirgar ababen hawa da kuma tsannanta bincike a gabar yammacin kogin Jodan