Iran ta yi Allah wadai da hare-haren da ta danganta da na ta’addanci na gwamnatin Amurka, wadanda ta ce sun karya dokokin kasa da kasa da kuma tsagaita wuta mai rauni da aka cimma don kawo karshen yaki a yankin.
A sanarwa da ma’aikatar Harkokin Wajen Iran ta fitar a wannan Alhamis bayan da Amurka, a rana ta biyu a jere, ta kai hare-haren sama kan Iran, ta ce ba wai kawai sun zama keta Dokar Majalisar Dinkin Duniya da ka’idojin dokokin kasa da kasa da hurimun kasar, a’a har ma sun sanya tsagaita wuta ta ranar 8 ga Afrilu ta zama ba ta da fa’ida.
Bugu da kari, Ma’aikatar ta tunatar da dukkan kasashen yankin game da alhakin da ya rataya a wuyansu na hana Amurka amfani da yankinsu domin kai hari kan Iran.
Ma’aikatar Harkokin Wajen ta Iran ta jaddada nauyin da ke kan dukkan kasashe membobin Majalisar Dinkin Duniya na yin adawa da keta ka’idodi da manufofin Yarjejeniyar Majalisar Dinkin Duniya da Amurka da gwamnatin Sahiyona suka yi.