Shugaban Kasar Iran ya bayyana cewa: Jagora da ya yi shahada kodayaushe yana jaddada ruhin ‘yan’uwantaka tsakanin al’umma da gwamnatocin Iran da Iraki
Shugaba Masoud Pezeshkian ya nuna godiyarsa ga jana’izar girmamawa da aka yi wa jagoran juyin juya halin Musulunci, Ayatollah Seyyed Ali Khamenei, a Iraki. Ya jaddada cewa: Jagoran da ya yi shahada ya ci gaba da jaddada ruhin ‘yan’uwantaka tsakanin mutane da gwamnatocin Iran da Iraki, yana mai bayyana fatansa na cewa dangantaka tsakanin kasashen biyu za ta fadada da zurfafa bisa ga dangantakar ‘yan’uwantaka, al’adu da addini da aka kafa.
A cewar kamfanin dillancin labarai na Iran IRNA, Shugaban ya aika da sakon godiya da jinjina ga gwamnati da al’ummar Iraki, yana yaba wa jana’izar girmamawa da aka yi wa jagoran juyin juya halin Musulunci a kasar Iraki.
A cikin sakonsa, Shugaban kasar Iran ya rubuta cewa: “Yana mika godiya da jinjinawansa ga ‘yan uwana, Shugaban Iraki Nizar Amidi da Fira Minista Ali Faleh al-Zaidi, da kuma jami’an wannan kasa, musamman manyan mutanen Iraki tare da wayewarsu mai tsawon lokaci, da kuma hukumomin addini da malamai wadanda suka karbi bakwancin gawar jagoran juyin juya halin Musulunci da ya yi shahada a harin wuce goda da iri.”