Ibrahim Nakha’i: Iran Za Ta Mayar Da Martani Mai Karfi Akan Duk Wata Wautar “Isra’ila”.

Dan majalisar Iran Ali Asgar Nakha’i ya shaida wa tashar talabijin din al-mayadeen cewa; Har yanzu Iran ba ta yi aiki da cikakken karfin da take da shi na makamai masu linzami ba, tare da yin gargadin cewa; Idan wani sabon fadan ya sake barkewa to makiya za su kasar da za ta shiga tarihi. […]
New York Times: An Bayyana Amurka A Matsayin Fatalwa

Wani marubuci dan kasar Amurka kasar Amurka a jaridar ” New York Times” mai suna Stephen Marche ya bayyana cewa; Amurka ta zama daidai da fatalwa a fagen siyasar kasa da kasa, duk da cewa tana karfi amma ba ta iya tabbatar da zaman lafiya mai dorewa a duniya. Marubucin ya kuma yi Ishara da […]
Senegal: Kotun Tsarin Mulki Ta Yi Watsi Da Kudurin Majalisa Na Rage Karfin Shugaban Kasa

Kotun tsarin Mulki ta kasar Senegal ta yi watsi da wani kuduri na majalisar dokokin kasar wanda yake nufin kayyade karfin ofishin shugaban kasar da kuma karfafa majalisar dokoki. A jiya Alhamis ne dai kotun tsarin mulkin da ita ce cibiyar shari’a mafi karfi a kasar Senegal ta soke kudurin da majalisar dokokin kasar ta […]
Rasha Ta Yi Wa Kasar Mozambique Tayin Taimaka Mata Ta Magance Ta’addanci

Ministan harkokin wajen kasar Rasha Sergey Lavrov wanda yake ziyarar aiki a kasar Mozambique ya yi wa gwamnatin kasar tayin taimaka mata ta magance barazar ta’addanci da take fuskanta. Sojojin kasar ta Mozambique dai suna fada da ‘yan ta’adda a yankin Arewacin kasar na Cabo Delgado dake da arzikin man fetur. Yankin ya fuskanci hare-hare […]
An Sanya Jagora Shahid A Makwancinsa Na Karshe Bayan Gagarumar Bankwana A Iran Da Iraki

An sanya gawar jagoran juyin juya halin musulunci Imam Sayyid Aliyul Khaminaei, a makwancinsa na kasarshe kusa da hubbaren Imam Aliyu bin Musa Arrudha da ke arewa maso gabacin kasar Iran bayan kwanaki na tarurrukan bankwana da salloli a Tehran, Qom da kuma kasar Iraki a safiyar Yau Jumma’a. Kamfanin dillancin labaran tasnim na kasar […]
Aragchi Ya Godewa Iraki Kan Gagarumar Jana’iyar Da Aka Yiwa Jagora Imam Khaminaei(Q)

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbas Aragchi ya godewa mutanen kasar Iraki da gwamnatin kasar kan gagarumin tarba da kuma jana’izar da suka yiwa jagora Shahid Imam Aliyul Khaminaei, a biranen Najaf da Karbala. Kamfanin dillancin labaran Tasnim na kasar Iran ya nakalto Aragchi yana fadar haka bayan an kammala rakiyar gawaki masu tsarki na […]
Manyan Jami’an Diblomasiyyar Iran Da Saudia Sun Tattauna Sabbin Hare-Haren Amurka Kan Iran

Ministan harkokin wajen kasar Iran Abbasa Aragchi ya zanta ta wayar tarho tare da tokwaransa na kasar Saudia Faisal bin Farhan a jiya Alhamis inda suka tattauna dangane da hare haren da sojojin Amurka suka kai kan kasar Iran wadanda suka kai ga shahadar sojoji da kuma fararen hula. Kamfanin dillancin labaran IP na kasar […]
Ofishin Jakadancin Iran A Turkiyya Ta Yi Watsi Da Jawabin Bayan Taron Kungiyar NATO

A wani bayanin maida martani ga bayanin bayan taro na kungiyar tsaro ta NATO a birnin Ankara babban birnin kasar Turkiya, ofishin jakadancin Jumhuriyar musulunci ta Iran ta yi watsi da jawabin bayan taro na kungiyar dangane da shirin nukliyar kasar Iran da kuma kwace mashigar ruwa ta Hurmuz da ta yi. Kamfanin dillancin labaran […]
IRGC Ta Ce Makamai Masu Linzaminta Sun Fada Kan Cibiyar CENCOM A Yammacin Asia

Dakarun kare juyin juya halin musulunci a nan Iran IRGC sun bada labarin fadawar makamai masu linzamunsu kan sansanonin rundunar CENCOM na Amurka a kasar Jordan. Kamfanin dillancin labaran ISNA na kasar Iran ya nakalto majiyar ta IRGC na cewa, makaman sun fada kan sansanin sojojin sama na Amurka da ake kira Muwaffaq Salti Air […]