Wannan kalamai nasa sun zo ne a yayin wani kiran waya da ya yi da Firayim Minista mai jiran gado na Iraki, Ali Faleh al-Zaydi, a ranar Talata, inda shugaban Iran ya taya sabon Firayim Minista murnar nadin nasa, tare da yi masa fatan alheri a kokarin da zai yi na kafa sabuwar gwamnatin Iraki.
Pezeshkian ya bayyana fatansa cewa sabuwar gwamnatin Iraki, ta hanyar gwaninta da ƙwarewarta, za ta shawo kan matsalolin tattalin arziki, ta kuma share fagen samun wadata, kwanciyar hanki, da ci gaba mai girma.
Da yake kira ga haɗin kan yanki, shugaban ya ce Iran ba ta neman rigima da maƙwabtanta, kuma tana goyon bayan warware bambance-bambancen yanki, ciki har da waɗanda ke cikin Tekun Fasha, ta hanyar tattaunawa.
Da yake bayyana abubuwan da suka shafi yankin baki ɗaya, shugaban ya ce ɗaya daga cikin muhimman batutuwa a yau shi ne wajabcin kawo ƙarshen yaƙe-yaƙe da matsin lamba daga ƙasashen waje a yankin, yana mai nuni da cewa sabani da Amurka ke nunawa, ta hanyar neman matsin lamba mafi girma kan Iran yayin da take tsammanin tattaunawa, yana sa tattaunawa mai ma’ana ta gagara a ƙarƙashin barazana.
Ya bukaci a kawar da barazanar soji, yana mai cewa samun kwanciyar hankali mai dorewa yana buƙatar mutunta haƙƙoƙin Iran da kuma kawo ƙarshen manufofin tilastawa. Ya kuma jaddada cewa an kai wa Iran hari sau biyu a lokacin shirye-shiryen tattaunawa, kuma ya soki sabon tura sojoji yayin da ake ci gaba da tattaunawa.
Pezeshkian ya kuma sake jaddada aniyar Iran game da ayyukan nukiliya na lumana, yana mai jaddada cewa a koyaushe ƙasar a shirye take ta ba da cikakken bayyana gaskiya a cikin tsarin ƙasashen duniya. Ya ƙara da cewa ci gaban kimiyya da fasaha, ciki har da fannin magunguna, noma, masana’antu, da kimiyyar nukiliya, wata nasara ce ta ƙasa wadda Iran ba za ta yi watsi da ita ba.
Pezeshkian ya gayyaci al-Zaydi da ya ziyarci Tehran domin tattaunawa kan ƙarfafa dangantakar kasashen biyu.
A nasa bangaren, Firayim Ministan Iraki mai jiran gado ya jaddada aniyar Bagadaza na inganta dangantaka a fannonin tattalin arziki, siyasa, tsaro, da yanki.
Al-Zaydi ya ƙara da cewa ƙarfin Iran ya kasance muhimmi wajen yaƙi da ta’addanci, kuma yana da mahimmanci wajen samar da kwanciyar hankali a yankin.
Ya ce Iraki a shirye take ta sauƙaƙe tattaunawa tsakanin Iran da Amurka, yana mai fatan cewa, ta hanyar kokarin da kuma haɗin gwiwar ƙasashen yankin gaba ɗaya, za a kawo ƙarshen yaƙin da ake ciki a yanzu da wuri-wuri, kuma a warware batutuwan da suka rage.