Kwanaki uku bayan tsagaita wutar yaki a Lebanon, mutanen kudancin kasar da kuma yankin Bika’ suna komawa kauyukansu da garuruwansu tare da cewa an rushe musu gidaje.
Rahotannin da suke fitowa daga kasar ta Lebanon sun ce, tun ranar da aka sanar da tsagaita wutar yaki a Alhamis da dare ne, mutane su ka fara kama hanyoyin kudancin kasar da kuma yankin Bika’ duk da cewa an rusa gidaje da yawa a yankunan.