Martanin Farko Daga Kungiyar Hizbullah Kan Harin Yahudawan Sahayoniyya A Kudancin Birnin Beirut

Martanin farko da kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hizbullah ta mayar kan harin ta’addancin da haramtacciyar kasar Isra’ila ta kai kan yankin kudancin birnin Beirut na

Martanin farko da kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hizbullah ta mayar kan harin ta’addancin da haramtacciyar kasar Isra’ila ta kai kan yankin kudancin birnin Beirut na kasar Lebanon

A cikin wata sanarwa da ya fitar a yammacin jiya Talata, wakilin kungiyar Hizbullah a majalisar dokokin kasar Labanon Ali Ammar ya bayyana cewa: Kungiyar gwagwarmayar Musulunci ta Hizbullah ba za ta yi shiru kan duk wani hari da aka kai mata ba.

Bayanin wakilin kungiyar Hizbullah a majalisar dokokin kasar ta Lebanon ya zo ne bayan wani mummunan harin bam da sojojin gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila suka kai kan yankin Haret Hreik da ke yankin kudancin birnin Beirut fadar mulkin kasar Lebanon.

Jiragen saman yakin gwamnatin haramtacciyar kasar Isra’ila sun kai farmaki kan wani gini da ke yankin Haret Hreik da ke kusa da asibitin Bahman a kudancin birnin Beirut, a daidai lokacin da rahotannin farko-farko ke tabbatar da shahadan mutane biyu da kuma jikkatan wasu da dama.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments