Ma’aikatar kiwon lafiya ta kasar Lebanon ta sanar da cewa, mutane 15 ne su ka yi shahada tun daga lokacin da aka sanar da tsagaita wuta a tsakanin kasar da Haramtacciyar Kasar Isra’ila.
Sanarwar ta kuma ci gaba da cewa, a ranar juma’ar nan da ta wuce, hare-haren ‘yan sahayoniya sun kashe mutane 6 a kudancin kasar, yayin da wasu mutane 2 su ka jikkata.
An tsagaita wutar yaki ne a tsakanin Lebanon da Haramtacciyar Kasar Isra’ila, a matakin farko bayan da Iran ta sanar da cewa shi ne sharadin zuwanta Islambad domin ttataunawa.
A gefe daya kungiyar gwgawarmaya ta Hizbullah tana cigaba da mayar da martani akan hare-haren ‘yan sahayoniyar, tana mai jaddada cewa matukar suna kai hari, to su ma za mu mayar da martani.