Rundunar sojin Isra’ila ta ci gaba da killace garin Tell, dake kusa da Nablus, inda ta tsare sama da samarin Falasdinawa 40 a lokacin wani samame da ta kai a garin dake a yankin Yammacin Kogin Jordan da ta Mamaye.
Gidan rediyon Falasdinawa ya ruwaito cewa sojojin Isra’ila suna gudanar da bincike a duk fadin garin, yayin da suke kewaye da shi a kowane bangare.
Tumda farko a ranar Juma’a, Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu da Ministan Tsaron kasae Israel Katz sun ba da umarnin dokar matakin soja” a kauyukan Falasdinawa a yankin Yammacin Kogin Jordan da ta Mamaye, bayan wani hari kusa da matsugunin Havat Gilad da ya kashe sojojin Isra’ila biyu tare da raunata wasu uku.
A cewar majiyoyi da shaidu, yahudawa ‘yan kama wuri zauna sun kai hari kan al’ummomin Falasdinawa da dama a Gundumar Nablus, inda suka kona gidaje da sauran kadarorin Falasdinawa.
An kashe Falasdinawa hudu a ranar Juma’a a wani hari da ‘yan kama wuri zamna da sojojin Isra’ila suka kai a garin Tell, a cewar Ma’aikatar Lafiya ta Falasdinawa.
A cewar alkaluman hukuma na Falasdinawa, an kashe Falasdinawa 87 a Yammacin Kogin Jordan da aka mamaye tun farkon 2026, ciki har da 21 yahudawa ‘yan kama wuri zaman na Isra’ila.
A watan Yulin 2024, Kotun Duniya ta ayyana ci gaba da kasancewar Isra’ila a yankin Falasdinawa da aka mamaye da cewa haramtacce ne kuma ta umarce ta da ta dakatar da duk wani sabon aikin gina matsugunni.