Jakadan Iran a Majalisar Dinkin Duniya ya ce: Duk wani hari kan kasarsa zai sanya sansanonin makiya su fuskanci hare-haren daukan fansa
Jakadan Iran kuma Wakilin Dindindin a Majalisar Dinkin Duniya, Amir Sa’ed Irawani, ya bayyana cewa: Kasarsa ba za ta fara wani yaki ba, amma za ta mayar da martani mai zafi kuma kwatankwacin yadda ta fuskanta. Amir Irawani ya yi wannan bayanin ne a cikin wata wasika da ya aika wa babban Sakataren Majalisar Dinkin Duniya António Guterres da Shugaban Kwamitin Tsaron Majalisar.
Wasikar, wacce aka aika a ranar Alhamis ta tabbatar da cewa: Ci gaba da barazanar da jami’an Amurka ke yi na amfani da karfi, gami da kalaman Shugaban Amurka game da yuwuwar amfani da Diego Garcia don kai hari kan Iran, ya zama “keta yarjejeniyar Majalisar Dinkin Duniya da dokokin kasa da kasa,” kuma yana iya jefa yankin cikin wani sabon zagaye na rikici da rashin zaman lafiya.
Irawani ya jaddada cewa: Ba za a iya yin watsi da kalaman Shugaban Amurka a ranar 18 ga Fabrairu, 2026, inda ya yi barazanar amfani da Diego Garcia da sauran wuraren soja idan ba a cimma yarjejeniya da Iran ba, a matsayin maganganu kawai. Maimakon haka, suna nuna babbar barazanar karfi, idan aka yi la’akari da yanayin yankin da ke da rauni da kuma ayyukan sojojin Amurka da ke ci gaba da gudana.