Iran Ta Bukaci Mdd Tayi Tir Da Harin Da Amurka Takai A Kasar Iran

hare haren da amurka ta kai kan gidan biki a kudancin iran keta dokokin kasa da kasa ne

Gholamhussain Darzi jakadan kasar iran a majalisar dinkin duniya ya bukaci kwamitin tsaro na majalisar donkin duniya da yayi tir da harin da kasar Amurka takai kan masu bikin aure a kudancin kasar iran                  da ya kai ga shahadar mutane 5 ciki har da wani yaro na shekaru 4 da haihuwa da kuma jikkata sama da mutane 70.

Jakadan yayi wannan kiran ne acikin wasikar da ya aikewa sakatare janar din majalisar dinkin duniya Antonio Guterres  da kuma shugaban kwamitin tsaron na majalisar dinkin duniya, a jiya labara bayan sabbin hare haren da Amurka ta kai a lardunan dake kudancin kasar wanda yayi sanadiyar mutuwar mutane 18 tare da jikkata wasu guda 108

Har ila yau ya bayyana cewa an kai harin ne kan masu bikin aure , kuma yayi ishara da cewa amurka ta kai wasu hare hare a gidajen mutane a kauyen kouhestan da sirik a lardin hormozgan.

kasar iran ta yi tir da wannan mummunan hari da kasar Amurka ta kai yace kai hari kan fararen hula da gangan , keta dokokin kasa da kasa ne kuma ana daukarsa a matsayin laifin yaki.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted