Ministan Harkokin Wajen Iran Seyyed Abbas Araqchi, wanda ke Beijing don ganawa da kuma tattaunawa da jami’an China, ya yi magana ta wayar tarho da Ministan Harkokin Wajen Saudiyya Faisal bin Farhan a ranar Laraba da rana.
A cikin wannan tattaunawar, bangarorin biyu sun yi nazari kan sabbin abubuwan da suka faru a yankin kuma sun jaddada ci gaba da hanyar diflomasiyya da haɗin gwiwa tsakanin ƙasashen yankin don hana bullowar da kuma ƙaruwar tashin hankali.
A cewar IRNA, Ministan Harkokin Wajen ya isa Beijing da safiyar yau a matsayin shugaban tawagar diflomasiyya. A lokacin wannan tafiyar, Araqchi ya tattauna dangantakar ƙasashen biyu da ci gaban yankin da na ƙasashen duniya tare da takwaransa na China, kuma ya jaddada cewa Iran tana da gaskiya da riƙon amana a fannin diflomasiyya.