Sojojin Iran Sun Kama Yan Ta’adda 8 A Kudancin Kasar

aci gaba da kokarin da dakarun kare juyin musuluci ta iran ke yi sun kama yan taadda guda 8 a kudancin kasar

Rahotanni sun bayyana cewa dakarun kare juyin musulunci na kasar iran sun sanar da cewa sun kama yan ta’adda guda 8 da ke da alaka da kungiyoyin yan ta’adda a kudu masu gabashin kasar a wani samame da dakarun kare juyin musulunci suka kai a yankin sisistan Baluchistan,

Acikin wani bayani da ta fitar a yau alhamis  dakarun kare juyin sun ce cikin wadanda aka kama a kwai masu garkuwa da injiiyoyi masu kula da manyan ayyuka da ake gudanarwa a sistan baluchestan da kuma kai hari kan sojoji da yin fashi da makami  da kuma tsora ta mutane a tsaikiyar lardin

Yace haka zalika yan ta’addan sun kai hari kan ofisoshin yan sanda da wasu kamfanoni da dai sauran ayyukan ta’addanci a yankin,

Jami’an tsaron kasar iran sun dauki tsauraran matakai don tabbatar da zaman lafiya da tsaro a yankin na sisisatan baluchestan, dake da iyaka da kasashen Pakistan da Afghanistan da suke da yan taadda  masu yawa dake kai hari kan fararen hula da kuma jami’an tsaro a shekara bayan da suka wuce

Jama’ian tsaro sun rusa cibiyar gungun yan ta’adda a watan aprilu dake da alaka da kungiayr Jaish al-adl a yakar kasar, dake yankin sistan baluchestan  kuma sun kashe yan ta’adda da dama a wajen

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted