Iran Ta Yi Tir da Harin Amurka Kusa da Asibitin Yara Na Ahvaz

Tehran ta ce harin ya tilasta wa hukumomi su gaggauta kwashe daruruwan marasa lafiya marasa galihu kuma ya haifar da firgici ga yara da ke

Iran ta yi Allah wadai da harin da Amurka ta kai kusa da wani asibitin yara da ke yankin kudu maso yammacin birnin Ahvaz, inda ta kira shi “laifin yaki.

Tehran ta ce harin ya tilasta wa hukumomi su gaggauta kwashe daruruwan marasa lafiya marasa galihu kuma ya haifar da firgici ga yara da ke jinya a asibitin.

Mai magana da yawun Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Esmail Baghai ya ce wallafa a shafinsa na X cewa Asibitin Shahid Baghai, wanda ya kunshi cibiyar da ta kware kan maganin cutar kansar yara, an kwashe su cikin dare bayan harin jiragen saman Amurka a wani wuri da ke kusa.

Harin ya haifar da matukar damuwa ga marasa lafiya kuma ya kawo cikas ga kulawar lafiyarsu.

 “Wannan harin na rashin imani, wanda ya yi kama da na zaluncin da Isra’ila ta yi wa cibiyoyin kiwon lafiya, ya haifar da damuwa ga yaran da ke kwance a asibiti kuma ya tilasta wa hukumomi su gaggauta kwashe marasa lafiya 211 in ji shi.

“Wannan ya zama babban laifi na yaki na matsorata da aka aikata kan mutane marasa laifi,” in ji shi.

Mazauna Ahvaz sun ba da rahoton jin fashewar abubuwa da dama a daren Laraba bayan da jiragen saman Amurka suka kai hari kan unguwanni da dama a kudu maso yammacin birnin Iran, ciki har da yankunan da ke kusa da asibitin, a cewar majiyoyin yankin.

Tehran ta yi ikirarin cewa wadannan hare-haren sun karya yarjejeniyar fahimtar juna da bangarorin biyu suka sanya wa hannu a watan da ya gabata kuma tana mayar da martani ta hanyar kai hari kan sansanonin sojojin Amurka a kasashen yankin Tekun Farisa.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted