ICC ta ki amincewa da daukaka karar Isra’ila

Kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa ta yi watsi da daukaka karar da Isra’ila ta shigar kan sammacin da ta fitar a baya

Kotun hukunta manyan laifuka ta kasa da kasa ta yi watsi da daukaka karar da Isra’ila ta shigar kan sammacin da ta fitar a baya na kama Firaministan Isra’ila Benjamin Netanyahu da tsohon ministan tsaro Yoav Gallant. .

A watan Nuwamba ne, kotun ta fitar da sammacin bisa zargin aikata laifukan yaki da cin zarafin bil’adama a Gaza.

Sammacin ya fusata Isra’ila da Amurka, wadanda tun daga lokacin suka kakabawa manyan jami’an ICC din takunkumi.

Benjamin Netanyahu ya kira matakin a matsayin “mai nuna kyama ga Yahudawa.”.”

A cikin watan Mayu, Isra’ila ta bukaci kotun ta ICC da ta yi watsi da sammacin.

Kotun dai ta yi watsi da bukatar ne a ranar 16 ga watan Yuli.

Mako guda bayan haka Isra’ila ta nemi izinin daukaka kara kan hukuncin, amma alkalan kotun sun yanke hukunci a ranar Juma’a cewa “batun kamar yadda Isra’ila ta tsara, ba za a daukaka kara ba.”

“Saboda haka majalisar ta ki amincewa da bukatar,” in ji kotun ta ICC

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments