Wani jami’in kungiyar Hamas Harun Nasiruddin ya bayyana cewa, kutsawar da yahudawa ‘yan share wuri zauna suke yi a cikin masallacin Kudus yakin addini ne, kuma yana a karkashin kokarin da mayar da masallacin na yahudawa.
Nasiruddin ya kuma ce; Abinda yake faruwa yana nuni ne da tsattsauran ra’ayin ‘yan sahayoniya wanda kuma yake samun cikakken goyon bayan hukumar “Isra’ila”.
‘Yan share wuri zauna suna shiga cikin harabar masallacin Kudus daga lokaci zuwa lokaci, tare da yin ibadunsa na yahudanci.
Shi dai masallacin Kudus yana a matsayin na uku bayan masallacin Ka’aba da masalalcin Annabi ( a.s) a Madina.