Sudan ta mayar da martanin kan shawarar Amurka, tana mai jaddada cewa; dole ne a yi la’akari da muradun ƙasar
Gwamnatin Sudan ta sanar da cewa: Dole ne a yi la’akari da muradun ƙasar kuma ta tabbatar da cewa yaƙi zai ci gaba har sai an kawo ƙarshen tawayen, a matsayin martani ga shawarar Amurka na neman warware rikicin Sudan.
Khartoum ta bayyana cewa duk wani shawarwari na kawo ƙarshen yaƙin dole ne ya yi la’akari da muradun ƙasar da haɗin kai da kuma cikakken ‘yancin yankinta, tana mai jaddada cewa yaƙi zai ci gaba har sai an shawo kan tawayen.
Wannan ya zo ne yayin da Chadi ta rufe iyakarta da Sudan bayan rikicin da ya faru a garin Tine da ke kan iyaka, wanda ke barazanar kawo cikas ga isar da kayan agaji ga yankin Darfur.
Kanun labarai