Falasdinawa 6 Ne Suka yi Shahada Sakamakon Hari Da Jiragen Yakin HKI Suka Kai A Gaza

Majaliysar Asibirti a yankin gaza ta bayyana cewa a ci gaba da keta yarjejeniyar dakatar da bude wuta da aka cimma tsakanin hamas da isra’ila

Majaliysar Asibirti a yankin gaza ta bayyana cewa a ci gaba da keta yarjejeniyar dakatar da bude wuta da aka cimma tsakanin hamas da isra’ila  a kalla falasdinawa guda 6 sun yi shahada wasu da dama kuma sun jikkata biyo bayan hari da HKI ta kaddamar a yankin Gaza

Kamfanin dillancin labarai na falasdinawa WAFa ya nakalto cewa wani bafalasdine guda yayi shahada yayin da wasu da dama kuma suka jikata a yammacin jiya Asabar bayan da jirgin sama mara matuki na isra’ila ya kai hari a al-sabra  dake makwabtaka da yankin zirin gaza, a wani bangare kuma wasu falasdinawa guda biyu sun yi shahada a wani hari da isra’ila ta kai kan rufin wani gida a layin al-aqsa a yankin tel hawa dake makwabtaka da kudu maso yammacin zirin gaza

Wannan mataki yazo na kwana daya bayan da shugaban Amurka Donald trump ya sanar da cimma matsaya na abin da ya kira bord of peace da zai bada damar shiga bangare na biyu na yarjejeniyar da aka cimma na dakatar da bude wuta

kungiyar hamas ta ce za ta ajiye makamanta saboda ceto yankin Gaza amma bayan isra’ila ta dakatare da hare-haren da take kai wa, kuma ta janye  daga yankin baki daya kammar yadda aka  cimma a yarjejeniyar da aka kulla.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted