Wani ɗan siyasa ɗan ƙasashen Turai ya soki shirun da ƙasashen yamma suka yi game da laifukan da Amurka ta aikata a kan Iran
Tsohon dan Majalisar Tarayyar Turai Mike Wallace ya soki shiru da rashin daukar mataki na jami’an kasashen Yamma game da laifukan Amurka da ta’addancinta a kan Iran, yana mai kiransu abin tausayi.
Dan siyasar Ireland ya rubuta a shafin sada zumunta na X a ranar Laraba da yamma: “Amurka ta kai hari kan wani bikin aure a Iran. A martanin da ta mayar, Iraniyawa sun kai hari kan sansanonin sojojin Amurka a yankin Tekun Farisa.”
Ya kara da cewa: “‘Yan siyasa da kafofin watsa labarai na kasashen Yamma ba za su iya la’antar ta’addancin Amurka ba. Saboda suna da tsoro.”