A shafinsa na X kafin rangadin da zai yi, Araghchi ya rubuta cewa: “Zan fara rangadin zuwa Islamabad, Muscat, da Moscow a kan lokaci.”
Ya kara da cewa: “Manufar ziyarce-ziyarcena ita ce daidaita tsakaninmu da abokan huldarmu kan batutuwan da suka shafi ƙasashen biyu da kuma tuntuɓar juna game da abubuwan da ke faruwa a yankin.”
Ministan ya jaddada a cikin saƙonsa kafin fara rangadin: “Maƙwabtanmu su ne fifikonmu.”
Ministan zai fara rangadin zuwa Islamabad, Muscat, da Moscow a ranar Juma’a.
Zai gudanar da tuntuɓo tsakanin ƙasashen biyu da kuma tattauna abubuwan da ke faruwa a yankin, da kuma halin da ake ciki a yaƙin da Amurka da gwamnatin ta’addanci ta Isra’ila suka kakabawa Iran.