Ma’aikatan Lafiya na Falasɗinu sun gano gawarwaki na aƙalla mutum 42 a Khan Younis da ke kudancin Gaza, bayan da akarun Isra’ila suka janye daga yankin, a cewar hukumomin wajen.
Shugaban ofishin watsa labarai na gwamnatin Gaza Ismail Thawabta ya ce, an gano gawarwakin mutum 42 da aka kashe a cikin sa’o’i kadan da suka gabata.
“Muna sa ran adadin wadanda suka mutu zai ƙaru saboda har yanzu akwai gawarwaki da dama a ƙarƙashin ɓaraguzan ginin,” in ji shi.