HKI Ta Kashe Falasdinawa 8 A Gaza A Yau Asabar

Akalla falasdinawa 8 ne suka yi shahada sanadiyyar hare haren da sojojin HKI suka kai kan falasdinawa a zirin Gaza, a yayinda wasu da dama suka ji rauni, wanda kuma ya kawo yawan Falasdinawa wanda aka kashe a gaza tun ranar 7 ga watan Octoban shekara ta 2023 zuwa kimani 73,350. Kamfanin dillancin labaran shehab […]

Wani Babban Sojan Amurka Ya Bayyana Cewa Kasar Bata Da Makaman Kare HKI

Kwamandan sojojin Amurka a turai wato ‘ U.S. European Command’ ya fadawa ma’aikayar yakin Amurka PENTAGON kan cewa karancin garkuwan makamai a sashen sojojin ruwa na kasar ya sa shi dole ya zabi kare sojojin Amurka daga makaman masu linzami samfurin balistic na kasar Iran maimakon kare sojojin HKI. Jaridar washigton Post ta nakalto Janar […]

Iran Ta Gargadi Birtaniya Cewa Za Tayi Amfani Da Karfinta Wajen Kare Kanta

Ministan harkokin wajen kasar iran Abass Araqchi ya gargadi gwamnatin Birtaniya game da duk wani yunkuri na taimakawa wajen kai mata hari , kuma yayi wannan gargadin ne a wata tattunawa da yayi ta wayar tarho da takwaransa na kasar Birtaniya  Ed Miliband  a jiya jumaa. Haka zalika yayi ishara cewa karkashin dokokin kasa da […]

 Falasdinawa  2 Ne Suka yi Shahada Sakamakon Hari Sojojin Israila A Gaza

Jiragen sama marasa matuki na isra’ila sun kai hari a yankin Gaza kuma sun yi sanadiyar shahadar falasdinawa guda biyu a ci gaba da keta yarjejeniyar dakatar da bude wuta da suke yi , da kuma tattaunawar da ake yi tsakanin tel aviv da kuma kungiyar gwagwarmaya ta hamas yanzu   Majiyoyin labarai sun bayyana […]

Araqchi Ya Yi Gargadi Game Da Fari

Ministan Harkokin Wajen Iran ya bayyana cewa: Bullar Fari a Kudu maso Yammacin Asiya yana ba da dama don ƙarfafa haɗin gwiwa da ƙasashe maƙwabta Ministan Harkokin Wajen Iran Abbas Araqchi ya jaddada cewa: Fari da ke fuskantar Kudu maso Yammacin Asiya zai iya mayar da shi dama ta ƙarfafa haɗin gwiwa da ƙasashen da […]

Araqchi Ya Tattauna Da Takwarorinsa Na Indiya Da Birtaniya Ta Wayar Tarho

Ministan Harkokin Wajen Iran ya yi tattaunawa tahanyar wayar tarho da takwarorinsa na Indiya da Birtaniya A yammacin jiya Juma’a, Ministan Harkokin Wajen Iran ya yi tattaunawa ta hanyar wayar tarho daban-daban da takwarorinsa na Indiya da Birtaniya. Ministan Harkokin Wajen Iran Seyyed Abbas Araqchi ya tattauna dangantakar kasashen biyu da ci gaban yankin yayin […]

Rundunar IRGC Ta Sanar Da Kwace Jiragen Ruwa Biyu Saboda Sabawa Doka

Rundunar Tsaron Juyin Juya Halin Musulunci ta sanar da kwace jiragen ruwa biyu masu dauke da mai da suka karya yarjejeniya a mashigar tekun Hormuz Rundunar Tsaron Juyin Juya Halin Musulunci ta (IRGC) ta sanar da cewa: An kai hari kan jiragen ruwa guda biyu na mai kuma an kama su da sanyin safiyar jiya […]

Sojojin Yemen Sun Tilasta wa Jiragen Ruwan Saudiyya Canja Hanya

Kakakin Rundunar Sojin Yemen ya sanar da cewa: Sun tilasta wa jiragen ruwan Saudiyya guda 8 sauya hanyarsu a matsayin wani ɓangare na daidaiton “killacewa da killacewa” Rundunar Sojin Yemen ta sanar a ranar Juma’a cewa ta tilasta wa jiragen ruwan mai guda takwas na Saudiyya sauya hanya zuwa ga mashigar Good Hope, a matsayin […]