Hukumar Kula da Tashar Jiragen Ruwa ta Tekun Farisa ta sanar da cewa: Ba zai yiwu a gudanar da jigilar kaya ta mashigar ruwar Hormuz ba
Sanarwar Hukumar Tsaron Jiragen Ruwa ta Tekun Farisa a kan dandalin X ta sake jaddada cewa: Mashigar Ruwan Hormuz ya ci gaba da kasancewa a rufe saboda hare-haren da Amurka ke kai wa yankin.
Asusun Hukumar Tsaron Jiragen Ruwa ta Tekun Farisa a kan dandalin X ya wallafa wani sako yana mai bayyana cewa:
“Saboda tambayoyi da masu nema suka yi akai-akai, hukumar zata so sake fayyace cewa: Wucewa ta Mashigar Hormuz ba zai yiwu ba, saboda ci gaba da hare-haren da sojojin Amurka ke yi a yankin. Da zarar an dawo da kwanciyar hankali da zaman lafiya, za a sake dawo da duk aikace-aikacen bisa ga tsari da jadawalinsu, kuma za a bayar da izini daidai da haka.”