Iran Ta Yabawa Kasar Turkiyya Kan Dakatarda Harkokin Kasuwanci Da HKI

Ministan harkokin wajen kasar Iran Amir Hussain Abdullahiyan ya yabawa kasar Turkiya kan dakatar da huldar kasuwanci da HKI saboda kissan kiyashin da take yi a gaza. Ya kuma kara da cewa wannan makatin zai kara takurawa haramtacciyar kasar. Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Abdullahiyan yana fadar haka a lokacin ganawarsa […]
Yemen: Kungiyar Ansarullah Ta Gargadi HKI Dangane Da Kai Farmaki Kan Yankin Rafah Na Zirin gaza

Kungiyar Ansarullah ta kasar Yemen ta gargadi HKI kan duk wani harin da zata kaiwa Falasdinawa a garin rafah na zirin Gaza. Ta kuma kara da cewa idan ta kuskura ta yi hakan, to kuwa zata kara tsananta yaki a yankin. Muhammad Mufatteh shugaban kwamitin ‘al-aksa’ ya bayyana haka ga tashar talabijin ta Almasirah ta […]
Babban Sakataren MDD Ya Ce Bai Kamata A Yi Barazana Ga Ma’aikatan Kotun Duniya Ta ICJ Ba

Kakakin babban sakataren MDD Stéphane Dujarric ya bayyana cewa bai kamata a yi barazana ga ma’aikatan kotun duniya ta ICJ wadanda suke aikinsu a gaza ba. Tashar Talabijin ta Aljazeera ta kasar Qatar ta nakalto Stéphane Dujarric yana fadar haka a lokacinda yake jawabi ga yan jaridu a birnin NewsYork na kasar Amurka ya kuma […]
Gwamnatin Kasar Pakistan Ta Bayyana Cewa Amurka Bata Da Hakkin Umurni Ko Hanata Kyautata Dangantaka Da Iran

Ministan harkokin wajen kasar Pakistan ya bayyana cewa kasarsa ba zata bawa gwamnatin Amurka damar ta bada umurni ko ta hana dangantakar kasuwanci tsakanin Iran da Pakistan ba. Kamfanin dillancin labaran ISNA na kasar Iran ya nakalto Mohammad Ishak Dor yana fadar haka a jaridar Down ta kasar Pakistan a jiya Talata. Ya kuma kara […]
Iran Na Daga Cikin Kasashen Yan Kadan A Duniya Wadanda Suke Da Fasahar Jinyar Cututtukan Rashin Daukar Ciki A Wajen Mata

JMI tana daga cikin kasashe kadan a duniya wadanda suke da fasahar jinyar cutar rashin daukar ciki a wajen mata. Kamfanin dillancin labaran IRIB-News ya nakalto shugaban kungiyar likitocin masu jiyar cututtukan haihuwa da rashin haihuwa na Iran yana fadar haka a yau Laraba . Dar Hamid Chubineh ya kara da cewa a ayyukan bincike […]
Hamas: farmakin Isra’ila kan Rafah ba zai ba ta nasara kan Falastinawa ba

Shugaban kungiyar Hamas, Osama Hamdan, ya gudanar da wani taron manema labarai, inda ya tabbatar da cewa, farmakin da sojojin Isra’ila suka kai a Rafah, bas u fita lafiya ba kamar yadda suke tunani. Ya mai jaddada cewa kungiyar ta nuna sassauci matuka, da ingantacciyar hanya domin cimma yarjejeniyar tsagaita wuta. Shugaban kungiyar Hamas, Osama […]
Majalisar Dinkin Duniya za ta kada kuri’a kan amincewa da Falasdinu a matsayin mamba

A ranar Juma’a 10 ga watan Mayu ne ake sa ran babban taron Majalisar Dinkin Duniya zai kada kuri’a kan daftarin kuduri na amincewa da baiwa Palasdinu damar zama cikakkiyar mamba a majalisar. Wannan dai zai kasance wani ma’auni ne a duniya kan irin goyon bayan da Falasdinawa ke samu a yunkurinsu, wanda Amurka ta […]
Shugaba Raeisi ya bayyana ramuwar gayyar Iran a kan Isra’ila a matsayin abin alfahari

Shugaban kasar Iran Ebrahim Raeisi ya jinjinawa matsayin da kasar ta dauka na mayarwa Isra’ila da martani a matsayin abin alfahari. Raeisi ya bayyana hakan ne a wata hira da aka yi da shi kai tsaye ta gidan talabijin na kasar a daren ranar Talata yayin da yake karin haske kan bangarorin farmakin da aka […]
Gaza: Akalla Falastinawa 14 Sun Yi shahada A Wani Harin Isra’ila a Gabshin Rafah

Rahotanni daga yankin Rafah da ke kudancin zirin Gaza na cewa, ana ci gaba da dauki ba dadi tsakanin sojojin Isra’ila da ‘yan gwagwarmayar Falasdinawa a gabashin birnin. Haka nan kuma jiragen yakin Isra’ila sun kai hari kan hedikwatar karamar hukumar da ke kusa da kan iyaka da Masar da kuma gidaje, lamarin da ya […]
Iran Ta Yi Kakkausar Suka Kan Kutsen Da Isra’ila Ta Yi A Rafah

Iran ta yi kakkausar suka kan kutsen da Isra’ila ta yi a birnin Rafah dake kudancin Gaza duk da gargadin da kasashen duniya suka yi na cewa hakan zai haifar da bala’in jin kai. Kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar Nasser Kan’ani ya ce an dauki matakin ne da nufin yin zagon kasa ga kokarin da […]
Putin : Zan Kare ‘Yanci, Hurumi, Da Tsaron Rasha

Shugaba, Vladimr Putin, na kasar Rasha, ya ce zai kare yanci da hurimi da tsaron kasarsa da mutuncin gwamnatinsa. Shugaban ya bayyana hakan ne a yayin da ake rantsar da shi a wani sabon wa’adin mulki. Shugaba Putin ya fara wa’adi na biyar akan karagar mulki a wani bukin rantsar da shi a fadar Kremlin […]
Hamas : Farmakin Isra’ila A Rafah, Zai Kara Tsananta Bala’in Jin Kai A Yankin

Kungiyar gwagwarmayar Falasdinawa ta Hamas ta ce farmakin da Isra’ila ta kai a Rafah zai kawai kara tsananta bala’in jin kai a yankin da aka yi wa kawanya. A cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Talata, kungiyar ta ce kutsen da Isra’ila ta yi a mashigar Rafah na da nufin kawo cikas ga […]