Search
Close this search box.

Iran Ta Yabawa Kasar Turkiyya Kan Dakatarda Harkokin Kasuwanci Da HKI

Ministan harkokin wajen kasar Iran Amir Hussain Abdullahiyan ya yabawa kasar Turkiya kan dakatar da huldar kasuwanci da HKI saboda kissan kiyashin da take yi

Ministan harkokin wajen kasar Iran Amir Hussain Abdullahiyan ya yabawa kasar Turkiya kan dakatar da huldar kasuwanci da HKI saboda kissan kiyashin da take yi a gaza. Ya kuma kara da cewa wannan makatin zai kara takurawa haramtacciyar kasar.

Kamfanin dillancin labaran IP na kasar Iran ya nakalto Abdullahiyan yana fadar haka a lokacin ganawarsa da shugaban kwamitin aikin tare na majalisun dokokin Iran-Turkiyya wanda yake ziyarar aiki a nan Tehran.

Labarin ya kara da cewa Kayhan Turkmenoglu ya isa nan birnin Tehran tare da tawagarsa wacce ta hada da wasu yan majalisun dokokin kasar Turkiya a jiya Talata.

Abdullahiyan ya kara da cewa kasashen turkiyya da Iran kasashe biyu ne masu karfi a yankin wadanda kuma zasu iya taimaka wajen kyautata al-amuran tsaro  a yankin.

A nashi bangaren Kayhan Turkmenoglu ya yabawa kasar Iran da irin goyon bayan da take bawa al-ummar Falasdinu musamman a yakin da take fafatawa da sojojin yahudawa a Gaza.

Ya kuma yi allawadai da hare haren da HKI ta kai kan ofishin jakadancin Iran a birnin Damascus na kasar Siriya. Wanda ya kai ga shahadar manya manyan jami’an sojojin kasar.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Inline Feedbacks
View all comments