Tsohon Ministan Harkokin Wajen Iran ya jaddada bukatar cimma yarjejeniyar tsaro mai inganci tsakanin kasashen Musulunci
Tsohon Ministan Harkokin Wajen Iran Mohammad Jawad Zarif ya jaddada wajibcin cimma cikakkun yarjejeniyoyi na tsaro tsakanin kasashen Musulunci.
Zarif ya wallafa wannan mahanga tashi a wata mujalla kuma ya rubuta cewa: “Kamar yadda ya rubuta shekara guda da ta gabata a cikin labarinsa mai suna ‘Babban Kasar Isra’ila da Yankunan Kasashen Musulmi Masu Karfi,’ manufofin nuna wariyar al’umma da tsaurin ra’ayin ‘Babban Kasar Isra’ila,’ waɗanda shugabannin Yahudawan Sahayoniyya ke da’awa a fili a waɗannan kwanaki, sun bayyana buƙatar samar da cikakkun yarjejeniyoyin tsaro tsakanin ƙasashen Musulunci fiye da kowane lokaci.”