Hatami: Iran Za Ta Ci Gaba Da Yaki Har Zuwa Cikakkiyar Nasara

Babban hafsan hafsoshin sojojin Iran, Major General Amir Hatami, ya bayyana cewa Iran za ta ci gaba da yaki da makiyanta har sai ta cimma

Babban hafsan hafsoshin sojojin Iran ya sha alwashin yaki da makiya har zuwa cikakkiyar nasara a kansu.

Kamfanin dillancin labaran Tasnim na kasar Iran ya nakalton Major General Amir Hatami  yana fadar haka a jiya Lahadi a lokacinda yake jawabi a taron raya ranakun fursinonin yaki a kallafaffen yaki na shekaru 8 tsakanin Iran da Iraki. Janar Hatami ya yaba da yentattun yaki na shekarun farko na juyin juya hali.

Ya kuma bayyanasu a matsayin gwaraza na farko a kasar. Wadanda suka tsaga a gaban azzaluman shuwagabannin kasar Iraki na lokacinda, wadanda kuma suke samun taimakon dukkan manya manyan kasashen duniya a lokacin.

Kallafeffen yaki na shekaru 8 bayan nasarar juyin juya halin musulunci, abin alfakhari ne ga duk wadanda suka sami halattarsa. Kuma yakin ya zama babban jarrabawa ga mutanen kasar Iran a lokacin saboda al-amura da suka zo daga baya.

Yace tsayawar matasan kasar Iran a gaban kasa Amurka, kasa mafi karfin makamai da tattalin arziki a duniya, wani babban al-amari ne wanda Jagora shahidai ya kodaitar a kansa, karkashin jagora na yanzu Aya. Mojtaba Khaminaei.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted