Rundunar Sojin Sudan Ta Ce: Sojojin Kasar Sun Fara Murkushe ‘Yan Tawaye A Birnin El-Fasher

Sojojin Sudan sun sanar da samun nasara kan ‘yan tawayen kasar na rundunar Rapid Support Forces a yakin garin El Fasher fadar mulkin jihar Darfur

Sojojin Sudan sun sanar da samun nasara kan ‘yan tawayen kasar na rundunar Rapid Support Forces a yakin garin El Fasher fadar mulkin jihar Darfur ta Arewa

Tashar talabijin ta Aljazeera ta watsa rahoton cewa: An yi arangama tsakanin sojojin Sudan da dakarun kai daukin gaggawa na Rapid Support Forces, a garin El Fasher fadar mulkin jihar Darfur ta Arewa, garin da aka kwashe makonni ana gwabza fada a cikinsa, wanda hakan ya haifar da damuwa ga kasashen duniya.

Rundunar sojin Sudan ta ce: Dakarun hadin gwiwar kungiyoyin masu dauke da makamai da sojojin kasar sun fatattaki abin da ta kira ‘yan ta’adda, dangane da kungiyar Rapid Support Forces, a wani gumurzu da aka yi a tsakaninsu a birnin El Fasher. Kuma rundunar sojin ta jaddada cewa: Sojojinta sun yi nasarar tarwatsa wasu motocin yakin ‘yan tawayen tare da kwace wasu.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted
Inline Feedbacks
View all comments