Shugaban kasar Iran ya gana da takwaransa na Afirka ta Kudu a gefen taron kolin kungiyar BRICS
Shugaban kasar Iran Mas’oud Pezeshkian ya gana da Shugaban kasar Afirka ta Kudu Cyril Ramaphosa a gefen taron kungiyar BRICS da aka yi a kasar Indiya, inda suka yi tattaunawar bangarorin biyu.
A cewar kamfanin dillancin labaran “IRNA” na kasar Iran, ya bayyana cewa: Ganawar da aka yi tsakanin Shugaba Pezeshkian da Ramaphosa ta gudana ne a gefen taron kungiyar BRICS. Za a fitar da Ζ™arin bayani game da tattaunawar daga baya.
Shugaba Pezeshkian ya isa kasar Indiya a safiyar Juma’a don halartar taron kungiyar BRICS na 18. A ranar farko ta ziyarar tasa, ya yi jawabi a babban taron, taron tattalin arziki, da kuma taron rufe taron, inda ya tattauna batutuwan da suka shafi shugabanci na duniya baki daya da kuma karfafa hadin gwiwa tsakanin bangarori daban-daban. Ya kuma gana da wasu shugabannin addinai, fitattun mutane, da shugabannin kasuwanci a Indiya.
Ya kuma gabatar da jawabi a taron BRICS Plus a ranar Lahadi, yana mai jaddada cewa: Bin ka’idojin dokokin kasa da kasa ba zai cika ba, ba tare da daukar matakin kasa da kasa mai karfi kan cin zarafin sojoji da kuma kai hari kan fararen hula ba. Ya kuma jaddada bukatar kunna rawar da kungiyar BRICS ke takawa wajen kare ikon mallakar kasa da kuma mutuncin yankuna, da kuma fuskantar manufofin da ke amfani da karfi.
Abin lura ne cewa: Shirin Shugaba Pezeshkian a lokacin ziyararsa ta kwanaki biyu ya kunshi jerin tarurruka da tattaunawa da wasu shugabanni da jami’ai da suka halarci taron.