Iran Tana Neman Adalci Kan Cin Zarafin ‘Yan Kasarta A Lamird Da Minab

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran ya jaddada cewa: Suna mai da hankali kan tsaron ƙasa da muradun ƙasa kuma suna neman cimma adalci ga shahidan

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran ya jaddada cewa: Suna mai da hankali kan tsaron ƙasa da muradun ƙasa kuma suna neman cimma adalci ga shahidan Lamird da Minab

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Isma’il Baqa’i ya bayyana harin makami mai linzami da Amurka ta kai a birnin Lamird a matsayin laifin yaki, inda ya lura cewa mutane 21 sun mutu yayin da wasu kimanin 180 suka jikkata a ranar 28 ga Fabrairu, wannan shekara ta 2026. Ya jaddada cewa: Jamhuriyar Musulunci ta Iran za ta ci gaba da neman adalci ga shahidan Lamird da Minab (a kudancin Iran).

Kamfanin dillancin labaran “IRNA” na Iran ya ruwaito cewa: Baqa’i ya gudanar da taron manema labarai a wurin da aka kai harin wuce gona da irin a birnin Lamird a lardin Fars, kudancin Iran, tare da halartar kafafen yada labarai na kasa da kasa. Wannan wani bangare ne na ziyararsa ta kwana daya zuwa Lamird, bayan duba wuraren zama da wani dakin wasanni da harin makami mai linzami na Amurka ya lalata a ranar 28 ga Fabrairu, 2026.

Mai magana da yawun Ma’aikatar Harkokin Waje ya gode wa jami’an Lardin Fars da Lamird (a kudancin ƙasar) kuma ya nuna godiyarsa ga kafofin watsa labarai na gida da na ƙasashen waje waɗanda suka kasance a yau a tituna da lunguna na Lamird, kuma suka shaida tasirin da alamun barna da makamai masu linzami na Amurka suka yi.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted