Wani mutum daya ya mutu kuma ma’aikacin jirgin ruwa ne sannan wasu ‘yan kasuwa hudu sun ji rauni bayan da wani makami ya bugi jirginsu a mashigar ruwan Hormuz
Hossein Amir Teymouri ya ruwaito cewa: Wani jirgin ruwa na Iran ya fuskanci bugu daga wani makami mai linzami da ba a san asalinsa ba, kusa da Tsibirin Hengam a Mashigar Hormuz a safiyar Lahadi, wanda ya yi sanadiyyar mutuwar ma’aikacin jirgin guda daya tare da jikkata wasu hudu.
Kamfanin dillancin labaran “IRNA” na kasar Iran ya ruwaito daga Amir Teymouri yana cewa: Jirgin Ruwan yana tafiya a Mashigar Hormuz kusa da Tsibirin Hengam a lokacin da lamarin ya faru, kuma yana da ma’aikatan jirgin goma a cikinsa.
A cewar rahoton, wani ma’aikacin jirgin, Jamshid Rajabi, ya mutu, yayin da wasu hudu suka jikkata lokacin da makamin ya bugi jirgin ruwan.
Gwamnan lardin Qeshm ya tabbatar da cewa: Ana gudanar da bincike don gano yanayin lamarin, yana mai lura cewa har yanzu ba a san ko daga ina aka harbo makamin ba, kuma ba a fitar da wani karin bayani game da lamarin ba tukuna.