MDD ta yi wannan kiran ne na tsagaita wuyar yakin Sudan cikin gaggawa bayan wani hari da jirgi maras matuki da aka kai akan cibiyoyin kiwon lafiya da hakan ya kara jefa mutane cikin matsanancin yanayi.
Shugaban hukumar kare hakkin bil’adama ta MDDVolker Turk ya bayyana cewa; Da akwai fararen hula da dama a suke fuskantar irin wadannan hare-haren,sannan kuma ya yi kira da a kawo karshen tsoma bakin kasashen waje a cikin harkokin wannan kasa.
Masu aikin gudanar da bincike na MDD a kasar Sudan,sun ce sojojin kasar da kuma dakarun kai daukin gaggawa (RSF) suna amfani da jiragen sama masu cin dogon zango wajen kai hare-hare da hakan yake nuni da fadadar yakin zuwa wasu yankuna masu nisa.
A kudancin Kurdufan an kai hare-haren akan makrantar kananan yara da kuma asibiti wanda ya yi sanadiyyar rasuwar mutane 114 da su ka hada da kananan yara 60.
Haka nan kuma an kai wani harin akan asibitin koyarwa a yankin wanda ya ci rayukan mutane 70.
Masu binciken na MDD sun ce da akwai kwararan dalilai da suke tabbatar da cewa dukkanin bangarorin biyu da suke yaki suna karya dokoki da kuma yiyuwar aikata laifukan yaki.
Yakin kasar Sudan a tsakanin sojoji da kuma dakarun kai daukin gaggawa (RSF) ya yi sanadiyyar mutuwar dubun dubatar mutane da kuma jikkata wasu dubai, kamar yadda ya tilastawa miliyoyin mutane yin hijira a cikin gida da kuma kasashen makwabta.