Rahotanni sun bayyana cewa shuwagabanin kabilu da malaman addini da manyan masu fada aji da sauran alummar yankin sistan Baluchistan sun yi tir da kisan gillan da aka yi wa molavi Yousef Gorji fitattacen malamin ahlu sunnah a kasar iran
A cikin wani bayani da suka fitar a yau talata dukkan bangarorin da suka sanyawa hannu a takardar sun bukaci a gudanar da bincike don gano wadan suka aikata kisan gillan da kuma gurfanar da su gaban shari’a domin su fuskanci hukuncin danyen aikin da suka aikata
Haka zalika bayanin ya jaddada cewa akwai bukatar wayar da kan jama’a da kuma sadaukarwa, kuma ya yi gargadin cewa wadanda suka gudanar da kisan gillan sun yi shi ne don kulla makirci na haifar da rashin zaman lafiya da tsaro da kuma tarzoma musamman a yankin kudu maso gabashin kasar
Daga karshe sun ce babban burin makiya shi ne haifar da rashin tsaro shi yasa suka kashe fitaccen mutum kuma mai tasiri kuma mai kima, domin haifar da rarrabuwar tsakanin mutane don tarwatsa zaman lafiya a yankin baki daya.