Kungiyar NLC ta nemi gwamnati ta ragewa ƴan Najeriya Radadi

kungiyar kwadago ta yi kira ga gwamnati ta ragewa alummar najeriya radadin rayuwa saboda tashin farashin mai

Ƙungiyar Kwadago ta NLC a Najeriya ta bukaci gwamnatin kasar ta samar da wani kunshin rage radadi ga ma’aikata a ilahirin sassan kasar sakamakon yadda sake kara farashin man fetur ya haifar da hauhawar farashin kayayyaki.

Har ila yau NLC  ta bukaci gwamnatin Najeriyar ta gabatar da wasu tsare-tsare da zasu taimaka wajen rage yawaitar hauhawar farashin na man fetur, tare da tabbatar da ganin ana sayar da danyen man ga matatun cikin gida a takardar kudi ta naira maimakon dala.

 A cikin wata sanarwa da ta fitar dauke da sa hannun shugabanta na kasa, Joe Ajaero ta ce wajibi ne gwamnatin ta daukin matakin rage radadin da tsadar man ke haifarwa ga al’ummar kasar musamman ma’aikata. A manyan biranen Najeriyar ana sayar da kowacce lita ta man fetur kan farashin naira dubu 1 da 430 a wani yanayi da bayanai ke cewa a wasu yankunan farashin ya haura haka, batun da NLC ke cewa tashin farashin man zai sake tsawwala rayuwa ga jama’ar kasar.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted