Rahotanni sun bayyana cewa kasar iran ta musanta jita-jitar da kasar Sweden ta ke yadawa na cewa kasar iran ta bawa jami’in diplomasiyarta saoi 48 da ya bar birnin Tehran, a matsayin martani ga matakin da Stockholm ta dauka na hana wani jami’in diplimasiyar Iran ci gaba da gudanar da ayyukansa a kasar Sweden
A cikin bayani da ma’aikatar harkokin wajen kasar iran ta fitar a yau Alhamis tayi tir da matakin da kasar Sweden ta dauka na hana wani jami’in diplomasiyar iran a ofishin jakadancinta dake Stockhum ci gaba da ayyukansa, yace zargin da aka yi wa iran bashi da tushe ko kadan
Yace matakin da kasar Sweden ta dauka babu adalci a ciki kuma yayi hannun riga da dokokin kasa da kasa na tilastawa wani jami’in diplomasiyar iran dake aiki a ofishin jakadancinta da ya bar kasar Sweden ba tare da wani kwakkwaran dalili ba,
Kuma a lokaci guda gwamnatin kasar Sweden tana zargi mara tushe na hannun irin kan batutuwan da suka shafi tsaro a kasar ta, kuma tuni ma’aikatar harkokin wajen kasar iran ta yi watsi da wannan zargi kuma ta bayyana matakin na Sweden kan jaimi’in diplomasiyar iran a matsayin rashin adalci.