Kasuwanci Tsakanin Kasashen Iran Da Iraki Yana Kara Habaka

Kasar Iraki tana samun kashi 22 cikin 100 na kayayyakin da Iran ke fitarwa zuwa wajen kasarta, ban da batun harkar mai Shugaban Hukumar Raya

Kasar Iraki tana samun kashi 22 cikin 100 na kayayyakin da Iran ke fitarwa zuwa wajen kasarta, ban da batun harkar mai

Shugaban Hukumar Raya Tattalin Arzikin Iran da Iraki ya bayyana cewa: Kusan kashi 22% na fitar da kayayyaki daga Iran zuwa wajen kasar, kasar Iraki ce ke karban kayayyakin a cikin ‘yan shekarun nan.

Hassan Danaeifar, wanda ke magana a wani taro da masu fafutukar tattalin arziki a lardin Kerman-Shah a ranar Laraba, ya jaddada muhimmancin Iraki a harkokin kasuwancin waje na Iran, yana mai cewa: “Iraki ta ci gaba da kasancewa babbar abokiyar cinikayya ta Iran tsawon shekaru 15 da suka gabata.”

Ya kara da cewa: Iraki tana wakiltar muhimmiyar kasuwa ga Iran: “Iraki ta mamaye wani muhimmin kaso na samar da kayayyaki daga cikin gida na Iran a cikin ‘yan shekarun nan. Kason Iraki na fitar da kayayyaki daga waje na Iran ya kai kusan kashi 22% a cikin shekaru ashirin da suka gabata, kuma wannan adadi wani lokacin ya kai kashi 25% ko 26%.

Shugaban Hukumar Raya Tattalin Arzikin ya jaddada cewa: Ana ci gaba da kokari sosai don warware matsalolin cinikayyar waje da Iraki, idan aka yi la’akari da muhimmancin wannan kasuwa ga tattalin arzikin Iran.

Danaeifar ta kuma jaddada muhimmiyar rawar da lardin Kerman-Shah ke takawa a harkokin kasuwanci da Iraki, inda ta kara da cewa: “Kerman-Shah tana kan gaba a cikin lardunan Iran dangane da yawan fitar da kayayyaki zuwa Iraki.”

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted