Jagoran Juyin Musulunci Ya Nada Sabbin Kwamandoji Soji Guda 6 A Iran

jagoran juyin musulunci na Iran ya sanar da sunayen sabbin kwamadojin sojin kasar da aka nada

Rahotanni daga iran sun bayyana cewa jagoran juyin musulunci na Iran Ayatullah mujtaba hussain kahamina’I ya sanar da sunayen sabben manyan kwamandoji guda 6 na rundunar sojin kasar ciki har da kwamandan dakarun kare juyin musulunci na kasar iran

A cikin sakon da jagoran ya aike da shi a jiya litinin ya bayyana Majo Janaral Ali Abdullahi a matsayin sabon kwamandan hafsan sojojin kasar, sai kuma birgediya Janar Kiomars Haidari  a matsayin mataimakinsa, sai kuma Majo Janarar Ahmad Vahidi shi kuma an kara marasa mukami zuwa matsayin major janaral a matsayin babban kwamandan dakarun kare juyin musulunci na kasar iran, sai kuma major janaral Mostapha Izadi a matsayin mataimakinsa.

haka zalika Reyal Admiral Ali Ozamae an nada shi a matsayin kwamanda hafsoshin sojin ruwa na dakarun kare juyin musulunci sai kuma hujjatul Islam Hossain Taeb a matsayin shugaban hukumar dakarun sa kai na kasa wato Basij.

A daya bangaren kuma jagoran ya nada major Janaral Aliu Abdullahi a matsayin kwamandan hafsan hafsoshin sojojin kasar , bayan shahadar wanda ya gabaceshi major Ganaral Abdulrahim musawi a harin da Amurka da Isra’ila suka kawo.

Ayatullah sayyid mujtaba Hussain Khamina’I ya ce an yi wannan nadin ne saboda tunawa da shahadar musavi mai girma da daraja a hannun makiya isra’ila da Amurka da kuma nuna jinjina ga ayyukan da abdullahi yayi da kuma kwarewarsa.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted