Iran: Za’a Bude Hurmuz Idan Amurka Ta Amince Da Sharuddanta

iran ta shi alwashin ci gaba da rufe mashigar hurmuz har sai amurka ta amince da sharadinta

Babban jam’in tsaro na kasar iran ya bayyana cewa za’a bude mashigar Hurmuz a tekun fasha ne inda iran ta sanya tsauraran matakai kan jirgen ruwa dake zirga-zirga a wajen tun a farkon watan maris saboda hare-haren da Amurka da isra’ila ke kai wa iran , kuma zaa bude ta ne kawai duk lokacin da Amurka ta amince da sharuddan da iran ta shinfida

Muhsin Riza’I sabon shugaban majalisar koli ta tsaron kasa da aka nada a baya bayan nan ya shaidawa jakadan kasar rasha a Tehran ZONG PIYU a wata ganawa da suka yi a jiya talata cewa dole ne Amurka ta kawo karshen yaki da take yi da iran da ma sauran kawayenta a yankin, kuma ta saki dukkan kadarorinta da take rike da su,kafin a bude mashigar Hurmuz

Yace matukar kasar Amurka ba ta canza halayenta ta ba, kuma bata amince da sharuddan iran ba to mashigar Hurmuz za ta ci gaba da kasancewa a rufe ba zaa iya bude ta ba. kuma ya jaddada cewa iran da oman da sauran kasashen dake da baki a mashigar Hurmuz suka cimma matsaya game da batun yin zango a hanyoyin ruwa to wannan ba zai yi tasiri game da matakin da iran ta dauka na rufewa ko bude mashigar Hurmuz ba

Ana sa bangaren jakadan  kasar china a iran Zong piyo ya jaddada matsayin china na nuna adawa da hare haren da Amurka da isra’ila ke kaiwa kasar iran, yace shugaban china xi jinping ya sanya wasu tsare-tsare guda 4 na samar da zaman lafiya da tsaro a yammacin Asiya

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted