Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Pakistan ya bayyana cewa: Ziyarar Ministan Harkokin Cikin Gidan Pakistan ya kai zuwa Tehran ta zo ne a cikin tsarin ci gaba da tattaunawa da Iran don zaman lafiya a yankin
Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Pakistan Tahir Andarabi ya tabbatar da ci gaba da kokarin da kasarsa ke yi na sauƙaƙa hulɗa tsakanin ɓangarorin da ke tattaunawa da kuma dawo da su cikin yarjejeniyar fahimtar juna ta Islamabad. Ya lura cewa ziyarar Ministan Harkokin Cikin Gida na Pakistan Mohsin Naqvi zuwa Tehran wani ɓangare ne na ci gaba da tattaunawa da Jamhuriyar Musulunci ta Iran don ƙarfafa dangantakar ƙasashen biyu da haɗin gwiwar tsaro, da kuma bayar da gudummawa wajen samar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.
Kamfanin dillancin labaran “IRNA” ya ruwaito cewa: Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Pakistan ya bayyana a yau, Laraba, a lokacin taron manema labarai na mako-mako a Islamabad, cewa: Pakistan tana hulɗa da dukkan ƙasashen ‘yan uwa a yankin, gami da ɓangarorin da suka rattaba hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna ta Islamabad. Ya jaddada cewa ƙoƙarin ƙasarsa ya mayar da hankali ne kan rage tashin hankali da kuma dawo da ɓangarorin biyu kan teburin tattaunawa.
Andarabi ya nuna ziyarar Ministan Harkokin Cikin Gida na Pakistan a Tehran jiya da kuma ganawarsa da manyan jami’an Iran, yana mai jaddada cewa “ziyarar ta zo ne a cikin tsarin shawarwarin ƙasashen biyu da nufin ƙarfafa dangantaka da haɗin gwiwar tsaro.”