Mataimakin Ministan Harkokin Wajen Iran ya bayyana cewa: Dole ne ƙasashen gabar Tekun Caspian su yi Allah wadai da ayyukan Isra’ila da Ukraine
Mataimakin Ministan Harkokin Wajen Iran Kazem Gharibabadi ya jaddada bukatar kasashen gabar tekun Caspian su yi Allah wadai da ayyukan Isra’ila da Ukraine.
Ya bayyana cewa dukkan kasashen gabar tekun Caspian ya kamata su yi Allah wadai da ayyukan ‘yan Sahayoniyya da Ukraine a Tekun Caspian tare da jaddada wajibcin girmama ikon mallakar kasa da kuma mutuncin yankuna.
Ya kara da cewa wadannan ayyukan ba wai kawai suna yin mummunan tasiri ga zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin ba ne, har ma suna nuna bukatar hadin kai tsakanin kasashen gabar tekun Caspian wajen kare tsaronsu na bai daya.