Rahotanni sun bayyana cewa Iran ta yi gargadi game da kokarin siyasantar da hanyoyin yin amfani da hukumar kula da makamashin nukiliya ta duniya, ta ce ana zargin darakta janar din hukumar da raunana matsayin hukumar da kuma yancinta , da kuma kokarin mayar da rahotonnin fasaha zuwa hujjar siyasa don tabbatar da hare haren soji da aka kai mata
A cikin bayanin da ya wallafa shafinsa na X kakakin ma’aikatar harkokin wajen kasar iran Esma’il Baqa’I yace hukumar makamshin nukuliya ta duniya ta dogra ne kan kwarewa kan fasaha da rashin nuna banbanci da kuma cin gashin kai , yace sai dai daraktan hukumar ya koma kamar wani sashi na hada rahotannin fasaha da hujjojin siyasa da kuma hada hujjojin da suka shafi yaki
Kakakin yayi gargadin cewa lamarin ya wuce batun lalata sunan hukumar kula da makamashin nukiliya ta majalisar dinkin duniya ko na babban darakattan hukumar , yace an tozarta babban abin da yake da muhimmancin ga hukumar wato aminci da ake da shi da ita a matsayinta na hukuma mai zaman kanta kuma mai adalci ga kowa