Firayim Ministan Iraki Mohammed Shia al-Sudani ya jaddada cewa wajibi ne a kan al’ummar Iraki kare ‘yancin kundin tsarin mulkin kasarsu wanda hakan ba zai yiwuwa ba sai hanyar tsara makomar kasar ta hanyar sahihin zaben ‘yan majalisar dokoki da ke tafe.
Al-Sudani ya jaddada cewa babu wani uzuri na kin kauracewa zabe da za a yarda da shi, yana mai bayyana cewa yin hakan “zai share fagen dawowar wadanda suka gaza da kuma wadanda suka ci hanci da rashawa.”
Ya ce, “Muna dogaro da shiga cikin harkokin zabe cikin sani da himma a ranar 11 ga Nuwamba, ranar da za mu tsara sabuwar makomar siyasa ta Iraki.”
Ya fayyace, “Muna son manufofin hikima da fifita muradun Iraki da al’ummar Iraki su ci gaba. Ba ma son komawa ga manufar haifar da rikici, mayar da martani cikin gaggawa, da kuma sanya Iraki cikin matsalolin ciki da waje.”
Al-Sudani ya nuna yanayin kwanciyar hankali da murmurewa, tare da alamu masu kyau ga tattalin arzikin Iraki, yana mai cewa “hanyar ci gaba ita ce aikin mafarki da kuma aikin mutane, wanda ya haɗa da damar saka hannun jari da ta wuce dala biliyan 450.”