Baqa’i: An Tabbatar Iran Ta Kai Hare-Hare Ne Kan Makiya Kai Tsaye

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran ya bayyana cewa: Takardar Qatar a Ƙungiyar Sadarwa ta Duniya ta tabbatar da daidaiton Iran wajen kai hare-haren daukan fasa

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran ya bayyana cewa: Takardar Qatar a Ƙungiyar Sadarwa ta Duniya ta tabbatar da daidaiton Iran wajen kai hare-haren daukan fasa ga wuraren sojin makiya

Kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran Isma’il Baqa’i ya rubuta a dandalin sada zumunta na X: “Ba kamar Amurka ba, wadda ta sanya kai hare-hare kan fararen hula a matsayin wani tsari na yau da kullun a cikin yaƙe-yaƙenta haramtattu, hare-haren kariya na Iran an kai su ne kawai kan wuraren soji. Rahoton hukuma ta Qatar ya tabbatar da wannan gaskiyar.”

Dangane da wannan, kakakin Ma’aikatar Harkokin Wajen Iran ya yi magana game da takardar da Qatar ta yi wa rijista tare da Ƙungiyar Sadarwa ta Duniya (ITU), wadda ta tabbatar da cewa: Hare-haren daukan fansa na kariya na Iran an kai su ne kan sansanonin sojojin Amurka kawai, yana mai cewa: “Qatar ta tabbatar a cikin wata takarda da aka gabatar wa ITU cewa: Hare-haren daukan fansa na kariya na Iran kan sojojin Amurka da ke zaune a ƙasar Qatar an kai su ne kawai kan wuraren sojin Amurka, kuma ba a kai hare-haren kan wani yanki na fararen hula ba.”

Ya ci gaba da cewa: “Bangaren da Qatar ta ambata kawai shi ne harin da aka kai kan wani wuri a ranar 18 ga Maris, amma ko a wannan yanayin, dole ne a yi la’akari da cewa wannan wurin yana hidimar kai hare-haren Amurka ne a kan Iran a lokacin.”

Ya ce: “Kwatanta wannan gaskiyar yana gwada adalci – daidaiton Iran wajen kai hare-hare – da ayyukan Amurka a hare-haren da ta kai wa fararen hula, makarantu, asibitoci, wuraren zama, bukukuwan aure, gadoji, da sauransu.”

Mai magana da yawun Ma’aikatar Harkokin Wajen ya jaddada cewa: akwai babban bambanci tsakanin al’umma mai wayewa wadda ta koyi muhimmancin bin ƙa’idodin ɗabi’a da na jin kai—ko da a cikin mawuyacin hali—da kuma masu mulkin mallaka waɗanda ke neman yaƙi kuma suka yi watsi da duk ƙa’idodin shari’a da na ɗabi’a a cikin nuna ikonsu da karfi.

Share

0 0 votes
Article Rating
Subscribe
Notify of
0 Comments
Oldest
Newest Most Voted