Iran da Qatar sun tabbatar da ci gaba da hadin gwiwa don hana karuwar tashe-tashen hankula a yankin
Ministan Harkokin Wajen Iran Abbas Araqchi da Fira Ministan Qatar kuma Ministan Harkokin Wajen kasar Sheikh Mohammed bin Abdulrahman Al -Thani sun yi magana ta wayar tarho a yammacin Talata.
A yayin kiran, bangarorin biyu sun tattauna sabbin abubuwan da suka faru a yankin, inda suka jaddada muhimmancin amfani da karfin diflomasiyya da kuma ci gaba da hadin gwiwa don hana karuwar rikici a yankin.